Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 4:3-10 in Hausa

Help us?

Yahaya 4:3-10 in Litafi Mai-tsarki

3 ya bar Yahudiya ya koma Galili.
4 Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya.
5 Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.
6 Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne.
7 Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha.”
8 Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.
9 Sai ba-Samariyar tace masa, “Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?” Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa.
10 Sai Yesu ya amsa yace mata, “In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai.”
Yahaya 4 in Litafi Mai-tsarki