Text copied!
Bibles in Hausa

Yahaya 3:10-17 in Hausa

Help us?

Yahaya 3:10-17 in Litafi Mai-tsarki

10 Yesu ya amsa yace masa, “Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba?
11 Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
12 Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama?
13 Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
14 Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum
15 domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada.
16 Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami.
17 Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa.
Yahaya 3 in Litafi Mai-tsarki