2 An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.