Text copied!
Bibles in Hausa

Luka 22:43-49 in Hausa

Help us?

Luka 22:43-49 in Litafi Mai-tsarki

43 Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
Luka 22 in Litafi Mai-tsarki