Text copied!
Bibles in Hausa

Luka 21:17-26 in Hausa

Help us?

Luka 21:17-26 in Litafi Mai-tsarki

17 Kowa zai ki ku saboda sunana.
18 Amma ba ko gashin kanku da zai hallaka.
19 A cikin hankurin ku za ku ribato rayukanku.
20 Sa'adda ku ka ga Urushalima tana kewaye da sojoji, sai ku sani da cewa faduwarta ta yi kusa.
21 Sai wadanda su ke Yahudiya su gudu zuwa kan tuddai, wadanda suke tsakiyar gari kuma su tafi, kada su bar wadanda suke kauyuka su shigo ciki.
22 Gama wadannan ranakun ramako ne, saboda duka abubuwan da aka rubuta su cika.
23 Kaiton wadanda suke da juna biyu da masu ba da mama a wannan kwanakin! Gama za a sha kunci mai girma a kasan, da fushi kuma zuwa ga mutanen nan.
24 Za su fadi ta kaifin takobi kuma za a kai su cikin bauta ga dukan kasashe, al'ummai za su tattake Urushalima, har ya zuwa lokacin al'ummai ya cika.
25 Za a ga alamomi cikin rana da wata da kuma taurari. A duniya kuma, al'ummai za su sha kunci, za su rude saboda rurin teku da rakuman ruwa.
26 Mutane za su suma da tsoro da kuma da tunanin abubuwa da za su abko wa duniya. Gama za a girgiza ikokin sammai.
Luka 21 in Litafi Mai-tsarki