Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 2:9-15 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 2:9-15 in Litafi Mai-tsarki

9 Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
10 cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
11 Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.”
12 Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, “Menene ma'anar wannan?”
13 Amma wasu suka yi ba'a suka ce, “Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.”
14 Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, “Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
15 Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
Ayyukan Manzanni 2 in Litafi Mai-tsarki