Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 2:33-40 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 2:33-40 in Litafi Mai-tsarki

33 Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
34 Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, “Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
35 har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.”'
36 Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
37 Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, “'Yan'uwa me za mu yi?”
38 Sai Bitrus ya ce masu, “Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
39 Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.”
40 Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, “Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.”
Ayyukan Manzanni 2 in Litafi Mai-tsarki