Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 2:15-21 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 2:15-21 in Litafi Mai-tsarki

15 Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
16 Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
17 Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
18 Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
19 Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
20 Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
21 Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
Ayyukan Manzanni 2 in Litafi Mai-tsarki