Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 19:13-18 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 19:13-18 in Litafi Mai-tsarki

13 Amma akwai Yahudawa masu tsubu da suka biyo ta wajen, suka dauka wa kansu su yi amfani da sunan Yesu. Suka ce, “Mun dokace ku cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa'azinsa, ku fita.”
14 Wadanda suka yi wannan su bakwai ne 'ya'yan wani babban firist Bayahude mai suna Siba.
15 Mugun ruhun ya amsa ya ce, “Na san Yesu, na san Bulus, amma ku, su wanene?”
16 Sai mugun ruhun da ke cikin mutumin ya fada a kan matsubatan ya fi karfinsu ya kuma bubuge su. Suka runtuma da gudu suka fice daga dakin tsirara da raunuka.
17 Wannan ya zama sanannen abu ga dukan mutane, Yahudawa da Helenawa mazaunan Afisa. Suka ji tsoro kwarai, sunan Ubangiji Yesu ya sami daukaka.
18 Masu bi da yawa kuma, suka zo suka furta mugayen ayyukan da suka aikata.
Ayyukan Manzanni 19 in Litafi Mai-tsarki