Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 16:2-11 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 16:2-11 in Litafi Mai-tsarki

2 Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan.
3 Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.
4 Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima.
5 Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.
6 Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya.
7 Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su.
8 Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.
9 Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. “Ka zo Makidoniya ka taimake mu”.
10 Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.
11 Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis;
Ayyukan Manzanni 16 in Litafi Mai-tsarki