Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 15:20-27 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 15:20-27 in Litafi Mai-tsarki

20 amma zamu rubuta masu da cewa, su guje wa gumaka da zina da faskanci da maye da cin mushe.
21 Tun zamanin da akwai mutane a kowanne birni wadanda suke wa'azi da karatun Musa a majami'u kowanne Asabaci.”
22 Sai ya yi wa manzanin kyau su da dattawa da dukan iklisiyar su zabi Yahuza da Barnaba da Sila da dattawan iklisiya a tura su Antakiya tare da Bulus da Barnaba.
23 Sai suka rubuta wasika, “Manzani da dattawa da 'yan'uwa zuwa ga al'ummai 'yan'uwa a Antakiya da Suriya da Kilikiya, gaisuwa mai yawa.
24 Mun ji cewa wasu mutane daga cikinmu wadanda ba mu umarce su ba, sun fita daga cikinmu sun yi maku koyarwar da ta daga maku hankali.
25 Ya yi kyau da dukanmu, muka amince mu zabi wadansu mutane mu tura su wurinku tare da Bulus da Barnaba,
26 mutane wadanda suka sadaukar da ransu domin sunan Ubangiji Yesu Almasihu.
27 Mun aika Yahuza da Sila su gaya maku wadannan abubuwa.
Ayyukan Manzanni 15 in Litafi Mai-tsarki