Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 13:38-44 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 13:38-44 in Litafi Mai-tsarki

38 'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai.
39 Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.
40 Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku:
41 'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku.”
42 Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa.
43 Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.
44 Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji.
Ayyukan Manzanni 13 in Litafi Mai-tsarki