Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 13:28-38 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 13:28-38 in Litafi Mai-tsarki

28 Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi.
29 Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.
30 Amma Allah ya tashe shi daga matattu.
31 Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.
32 Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu.
33 Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: “Kai da na ne yau na zama mahaifinka.”
34 Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: “Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu.”
35 Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.'
36 Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba,
37 amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.
38 'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai.
Ayyukan Manzanni 13 in Litafi Mai-tsarki