Text copied!
Bibles in Hausa

Ayyukan Manzanni 10:5-9 in Hausa

Help us?

Ayyukan Manzanni 10:5-9 in Litafi Mai-tsarki

5 “Yanzu ka aika mutane zuwa birnin Yafa su kawo mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus.
6 Yana zama tare da Saminu majemi, wanda gidansa ke bakin teku.
7 Da mala'ikan da ya yi magana da shi ya tafi, Karniliyas ya kira biyu daga barorin gidansa, da kuma soja guda mai bautar Allah daga cikin sojojin da suke masa hidima.
8 Karniliyas ya fada masu dukan abin ya faru sai ya aike su Yafa.
9 Washe gari wajen sa'a ta shida (tsakar rana) suna cikin tafiya da suka yi kusa da birni, Bitrus ya hau kan bene don ya yi addu'a.
Ayyukan Manzanni 10 in Litafi Mai-tsarki