Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 5

Yahaya 5:1-6

Help us?
Click on verse(s) to share them!
1Bayan haka akwai idi na yahudawa, kuma Yesu ya tafi Urashalima.
2To a cikin Urashilima kusa da kofar tumaki akwai tabki, wanda ake kira Baitasda da harshen Ibraniyanci, yana da shirayi biyar.
3Taron mutane dayawa masu ciwo da, makafi da guragu da shanyayyu suna kwance a wurin suna jira a dama ruwan.
4Gama mala'ikan Ubangiji kan sabko a cikin tabkin ya dama ruwan, wanda ya fara taba ruwan sai ya warke komai cutar da yake da ita.
5Akwai wani mutum a bakin tabki yana kwance yana da rashin lafiya har shekara talatin da takwas.
6Da Yesu ya gan shi yana kwance a wurin sai ya gane ya dade a wurin, sai ya ce masa, “Ko kana so ka warke?”

Read Yahaya 5Yahaya 5
Compare Yahaya 5:1-6Yahaya 5:1-6