Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 4

Yahaya 4:24-33

Help us?
Click on verse(s) to share them!
24Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya.”
25Matar ta ce masa, “Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu.
26Yesu ya ce mata, “Ni ne shi, wanda ke yi maki magana.”
27A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, “Me kake so?” Ko kuma, “Don me ka ke magana da ita?”
28Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen,
29“Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?”
30Suka bar garin suka zo wurinsa.
31A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, “Mallam, ka ci.”
32Amma ya ce masu, “ina da abinci da ba ku san komai akai ba.”
33Sai almajiran suka ce da junansu, “Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?”

Read Yahaya 4Yahaya 4
Compare Yahaya 4:24-33Yahaya 4:24-33