Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 3

Yahaya 3:27-35

Help us?
Click on verse(s) to share them!
27Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.
28Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
29Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan.
30Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
31Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa.
32Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa.
33Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
34Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba.
35Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa.

Read Yahaya 3Yahaya 3
Compare Yahaya 3:27-35Yahaya 3:27-35