Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 3

Yahaya 3:22-27

Help us?
Click on verse(s) to share them!
22Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma.
23Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma,
24domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
25Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa.
26Suka je wurin Yahaya suka ce, “Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa.”
27Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.

Read Yahaya 3Yahaya 3
Compare Yahaya 3:22-27Yahaya 3:22-27