Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 2

Yahaya 2:12-17

Help us?
Click on verse(s) to share them!
12Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”

Read Yahaya 2Yahaya 2
Compare Yahaya 2:12-17Yahaya 2:12-17