Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Yahaya - Yahaya 20

Yahaya 20:2-11

Help us?
Click on verse(s) to share them!
2Sai ta ruga da gudu zuwa wurin Saminu Bitrus tare da almajirin nan da Yesu ke kauna, tace masu, “Sun dauke Ubangiji daga kabarin, bamu kuwa san inda aka sa shi ba.”
3Sai Bitrus tare da almajirin nan suka fita, kuma suka tafi kabarin,
4dukansu suka ruga da gudu tare, amma daya almajirin ya riga Bitrus isowa kabarin,
5Sai ya sunkuya ya leka ciki, ya ga likkafanin lillin a wurin, amma fa bai shiga ciki ba.
6Sai Saminu Bitrus ya iso daga bayansa sai ya shiga kabarin, ya tarar da likkafanin lillin a ajiye.
7sai fallen kuma da yake kansa. Ba'a ajiye tare da likkafanin ba amma aka linkeshi aka ajiye shi daban.
8Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga ya gani, sai ya ba da gaskiya.
9Har ya zuwa wannan lokacin basu san nassin daya ce zai tashi daga matattu ba.
10Sai almajiran suka sake komawa gida kuma.
11Amma Maryamu tana tsaye a bakin kabarin tana kuka. Yayin da take kuka, sai ta sunkuya ta leka cikin kabarin.

Read Yahaya 20Yahaya 20
Compare Yahaya 20:2-11Yahaya 20:2-11