Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Romawa - Romawa 4

Romawa 4:5-10

Help us?
Click on verse(s) to share them!
5Amma kuma shi da bai da ayyuka kuma maimakon haka ya gaskanta ga wanda ke kubutar da masu zunubai, bangaskiyarsa an lisafta ta a misalin adalci.
6Dauda ya yi furcin albarka bisa mutumin da Allah ya lisafta mai adalci da rashin ayyuka.
7Sai ya ce, “Masu albarka ne wadanda aka yafe laifofinsu, kuma wadanda zunubansu a rufe suke.
8Mai albarka ne mutumin da ko kadan Ubangiji ba zaya lisafta zunubin sa ba.”
9To albarkar da aka fadi ko a bisansu wadanda aka yi wa kaciya ne kadai, ko kuwa a bisan su ma marasa kaciya? Domin mun yi furcin, “Bangaskiyar Ibrahim an lisafta ta adalci ce agare shi.”
10Yaya aka lisafta ta? Bayan Ibrahim ya yi kaciya, ko kuwa a rashin kaciya? Ba a cikin kaciya ba, amma a rashin kaciya.

Read Romawa 4Romawa 4
Compare Romawa 4:5-10Romawa 4:5-10