Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 6

Luka 6:27-32

Help us?
Click on verse(s) to share them!
27Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
28Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
29Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
30Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
31Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
32Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.

Read Luka 6Luka 6
Compare Luka 6:27-32Luka 6:27-32