Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 3

Luka 3:6-13

Help us?
Click on verse(s) to share them!
6kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
7Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
10Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
11Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
12Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
13Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”

Read Luka 3Luka 3
Compare Luka 3:6-13Luka 3:6-13