Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 24

Luka 24:14-20

Help us?
Click on verse(s) to share them!
14Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
15Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
16Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
17Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
18Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
19Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
20Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.

Read Luka 24Luka 24
Compare Luka 24:14-20Luka 24:14-20