Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 20

Luka 20:19-34

Help us?
Click on verse(s) to share them!
19Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
20Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
22Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24“Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
25Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
26Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
27Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
28suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
29Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
30haka ma na biyun.
31Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
32Daga baya sai matar ma ta mutu.
33To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
34Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure.

Read Luka 20Luka 20
Compare Luka 20:19-34Luka 20:19-34