Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 1

Luka 1:10-19

Help us?
Click on verse(s) to share them!
10Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.

Read Luka 1Luka 1
Compare Luka 1:10-19Luka 1:10-19