Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Luka - Luka 12

Luka 12:17-23

Help us?
Click on verse(s) to share them!
17ya yi tunani, ya ce, 'Me zan yi, domin ba ni da wurin da zan iya ajjiye amfanin gonata?'
18Sai ya ce, na san abin da zan yi. Zan rushe rumbuna na in gina wadansu manya-manya, a nan zan ajjiye hatsi na da dukan abubuwa.
19Sai in ce da raina, “Ya raina, kana da abu da yawa da aka ajjiye dominka, sai ka huta, ka ci, ka sha, ka yi murna.”
20Amma sai Allah ya ce da shi, 'Wawan mutum, a cikin daren nan ana son ranka daga wurinka. Kayan da ka tara ka shirya wa kanka, na wa za su zama?'
21Haka wanda ya tara wa kansa dukiya yake, idan ba shi da dukiya a wurin Allah.”
22Yesu, ya ce da almajiransa, “Saboda haka ina cewa da ku, kada ku damu da rayuwarku, wato, abin da za ku ci, ko abin da za ku sa a jikinku.
23Gama rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.

Read Luka 12Luka 12
Compare Luka 12:17-23Luka 12:17-23