Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Ayyukan Manzanni - Ayyukan Manzanni 8

Ayyukan Manzanni 8:7-12

Help us?
Click on verse(s) to share them!
7Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
8Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
9Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
10Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, “Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.”
11Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
12Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.

Read Ayyukan Manzanni 8Ayyukan Manzanni 8
Compare Ayyukan Manzanni 8:7-12Ayyukan Manzanni 8:7-12