Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Ayyukan Manzanni - Ayyukan Manzanni 2

Ayyukan Manzanni 2:1-12

Help us?
Click on verse(s) to share them!
1Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
2Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
3Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
4Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
5A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
6Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
7Suka yi mamaki matuka; suka ce, “Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
8Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
9Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
10cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
11Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.”
12Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, “Menene ma'anar wannan?”

Read Ayyukan Manzanni 2Ayyukan Manzanni 2
Compare Ayyukan Manzanni 2:1-12Ayyukan Manzanni 2:1-12