Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Ayyukan Manzanni - Ayyukan Manzanni 1

Ayyukan Manzanni 1:2-9

Help us?
Click on verse(s) to share them!
2har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, “Kun ji daga gare ni,
5cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.”
6Sa'adda suna tare suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7Ya ce masu, “Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.

Read Ayyukan Manzanni 1Ayyukan Manzanni 1
Compare Ayyukan Manzanni 1:2-9Ayyukan Manzanni 1:2-9