10Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin.”
11Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.
12Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a.
13Suna cewa, “Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu.”