Text copied!
CopyCompare
Litafi Mai-tsarki - Ayyukan Manzanni - Ayyukan Manzanni 15

Ayyukan Manzanni 15:5-9

Help us?
Click on verse(s) to share them!
5Amma wadansu mutane wadanda suka ba da gaskiya daga cikin Farisawa, suka tashi suka ce, “Dole ne a yi masu kaciya a kuma umarce su su kiyaye dokar Musa.”
6Sai manzanin da dattawan suka taru don su duba wannan lamari.
7Bayan mahawara mai tsanani, sai Bitrus ya tashi ya ce masu, “'Yan'uwa, kun san lokacin baya da ya wuce, Allah ya yi zabi a cikinku, cewa ta bakina ne al'ummai za su ji bishara, su kuma ba da gaskiya.
8Allah, wanda ya san zuciya, ya yi masu shaida, ya kuma basu Ruhu Mai Tsarki kamar yadda ya yi mana;
9kuma bai bambanta mu da su ba, ya tsabtace zuciyarsu ta wurin bangaskiya.

Read Ayyukan Manzanni 15Ayyukan Manzanni 15
Compare Ayyukan Manzanni 15:5-9Ayyukan Manzanni 15:5-9